fidelitybank

An kori ƴan sanda bakwai daga bakin aiki

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Imo, ta kori jami’anta bakwai waɗanda aka samu da laifukan da suka ƙunshi cutar da al’umma da razanarwa da yi wa jama’a ƙwacen kuɗi, da bincikar wayoyin jama’a ba bisa ƙa’ida ba, tare kuma da saɓa wa umarnin babban Sifeton ‘yan sanda na ƙasar kan kyakkyawar mu’amala da sauran al’umma.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Mike Abattam ya fitar, ya ce an kama jami’an ne ranar 8 ga watan Nuwamban 2022 a harabar wani banki da ke birnin Umuahia na jihar Abia, a lokacin da suke tsaka da aikata munanan laifukan karɓar kuɗi a wajen mutanen da ba su aikata wani laifi ba.

Ya ƙara da cewa an gurfanar da su a gaban kotun Majistare da ke birnin Owerri, inda aka same su da laifi, inda kuma nan take rundunar da kore su daga bakin aiki.

Mista Abattam ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar ya bayar da umarni ga duka shugabannin ofisoshin ‘yan sanda da ke faɗin jihar da su tabbatar da cewa sun gargaɗi jami’an da ke aiki a ƙarƙashinsu kan aikata makamancin wannan laifi,.

Yana mai cewa duk jami’in ɗan sandan da aka samu da hannu a irin wannan laifi to zai fuskanci matakin ladabtarwa.

www.legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...
X whatsapp