fidelitybank

An kori ƴan sanda bakwai daga bakin aiki

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Imo, ta kori jami’anta bakwai waɗanda aka samu da laifukan da suka ƙunshi cutar da al’umma da razanarwa da yi wa jama’a ƙwacen kuɗi, da bincikar wayoyin jama’a ba bisa ƙa’ida ba, tare kuma da saɓa wa umarnin babban Sifeton ‘yan sanda na ƙasar kan kyakkyawar mu’amala da sauran al’umma.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Mike Abattam ya fitar, ya ce an kama jami’an ne ranar 8 ga watan Nuwamban 2022 a harabar wani banki da ke birnin Umuahia na jihar Abia, a lokacin da suke tsaka da aikata munanan laifukan karɓar kuɗi a wajen mutanen da ba su aikata wani laifi ba.

Ya ƙara da cewa an gurfanar da su a gaban kotun Majistare da ke birnin Owerri, inda aka same su da laifi, inda kuma nan take rundunar da kore su daga bakin aiki.

Mista Abattam ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar ya bayar da umarni ga duka shugabannin ofisoshin ‘yan sanda da ke faɗin jihar da su tabbatar da cewa sun gargaɗi jami’an da ke aiki a ƙarƙashinsu kan aikata makamancin wannan laifi,.

Yana mai cewa duk jami’in ɗan sandan da aka samu da hannu a irin wannan laifi to zai fuskanci matakin ladabtarwa.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp