Babban bankin kasa CBN ya kori ma’aikata sama da 100 cikin abin da bai gaza kwana 20.
BBC ta gano lamarin ya shafi sassan bankin da dama, amma ya zuwa yanzu an fara korar ne daga sashe uku.
Wadanda lamarin ya shafa yawancinsu masu manyan matsayi ne a CBN.
Yanzu mafi yawan ma’aikatan bankin cikinsu ya É—uri ruwa saboda rashin sanin mai gobe za ta haifar.
Babu dai wanda ya yarda BBC ta naÉ—i muryarsa kan lamari, wasu na cewa ko hukumomin bankin ba za su iya cewa komai ba saboda rashin sanin inda aka dosa.
CBN na ci gaba da bincike kan badaƙalar da aka tafka tun daga wasu shekaru da suka wuce baya.
Bayanai na cewa waɗan nan binciken da aka yi ba su shafi ɓangaren kuɗaɗen ketare ba da sauya fasalin naira, wanda anan gana ake tsammanin za a je kansu.