A ranar Lahadin da ta gabata ne aka dakatar da Sarkin Yandoton Daji, Aliyu Marafa, a jihar Zamfara, bayan da ya danka wa wani dan ta’adda da ake nema ruwa a jallo, mai suna Ada Aleru, Sarkin Fulanin (shugaban Fulani) na masarautar.
Gwamnan jihar Bello Matawalle ya kafa masarautar Yandoton Daji daga masarautar Tsafe a ranar 18 ga watan Mayu.
Yayin da yake samar da masarautun, gwamnan ya bukaci sabon sarkin da ya yi amfani da sabbin damar da aka samu a kofar gidansu wajen kara samun hadin kai tare da kara cusa hadin kai da da’a a cikin al’umma kamar yadda ya gada daga kakanninmu.
Yankin da zai yi tasiri a sabuwar masarauta ya kunshi Yandoton Daji, Keta, Kizara, Bawa Kwanga, Kwaren Ganuwa, Danjibga, da Kuncin Kalgo dake da hedikwata a Birnin Yandoto.
Sai dai bayan wata biyu da kafa masarautar, an dakatar da Mista Marafa bayan ya ba da sarautar gargajiya ga wanda ake nema ruwa a jallo, Mista Aleru.
Sai dai ba shi ne basaraken gargajiya na farko da ya shiga hannun gwamnatin jihar bisa zargin taimakawa ayyukan kungiyoyin ‘yan ta’adda a jihar ba.
Tun a shekarar 2019, gwamnan ke zargin sarakunan gargajiya a jihar da hada baki da kungiyoyin ‘yan ta’adda da ke kai hare-hare a cikin al’umma, cibiyoyin ilimi, da ofisoshin gwamnati a jihar. Su kuma ‘yan bindigar sun kware wajen yin garkuwa da matafiya domin neman kudin fansa.
Bayan haka, gwamnan ya kori ko kuma dakatar da wasu daga cikin sarakunan bisa zargin taimakawa ayyukan kungiyoyin ta’addanci. Sai dai babu daya daga cikin wadanda aka kora da aka tuhume su da aikata wani laifi.
Ga wasu daga cikin sarakunan gargajiya da aka dakatar ko kuma aka tsige su bisa zargin tallafa wa ‘yan ta’adda a jihar.