fidelitybank

An kori Minista sakamakon cire tallafin man fetur

Date:

Shugaban Angola João Lourenço ya kori ministan kula da harkokin tattalin arziki da kyautata rayuwar al’umma sakamakon zanga-zangar da ta ɓarke bayan matakin gwamnati na cire tallafin man fetur.

Ya maye gurbin Manuel Nunes Júnior, ƙwararren minista kuma farfesa kan tattalin arziki, da gwamnan babban bankin ƙasar, Jose de Lima Massano, a cewar wata sanarwa.

Cire tallafin – wanda Mista Nunes Júnior ya ce an yi ne don rage kuɗaɗen da gwamnati ke kashewa – ya fara aiki ranar 1 ga watan Yuni, abin da kuma ya sa farashin man ya hauhawa.

Tuni zanga-zanga ta ɓarke a ƙasar mai arzikin fetur, inda ake sa ran za ta ƙaru a ranakun ƙarshen mako.

A ranar Litinin, mutum biyar sun mutu sannan wasu takwas suka jikkata bayan ‘yan sanda sun buɗe wuta kan masu zanga-zanga a garin Huambo.

Angola na cikin ƙasashen da suka fi arzikin man fetur a Afirka.

sunnnewspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp