fidelitybank

An kori Dan Sandan da aka kama da satar Jarirai

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas, ta amince da korar Sufeto Samuel Ukpabio, bisa zargin satar jarirai.

Da yake sanar da korar jami’in a wata sanarwa da ya fitar a shafin sa na Twitter da aka tabbatar, mai magana da yawun rundunar, SP Benjamin Hundeyin ya bayyana cewa an amince da korar jami’in ne a ranar Alhamis domin share fagen gurfanar da shi.

Ya ce kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Idowu Owohunwa, ya sake jaddada aniyarsa ta ‘yan sandan Legas bisa ka’idojin doka, wayewa da mutunta ran dan Adam.

Ku tuna cewa wata mata ‘yar shekara 35 mai suna Fortune Ohafuoso, ta zargi Ukpabio, wacce ke aiki a Panti Division, da hada baki da wasu don sace jaririn ta na rana.

Mahaifiyar mai yara uku ta bayyana cewa Ukpabio ta kama ta kuma ta zarge ta da yunkurin siyar da jaririyar a kan N3m kuma ya tilasta mata ta rubuta sanarwa a kan hakan.

Obhfuoso ya yi ikirarin cewa Ukpabio da karfin tsiya ta kwashe sabon jaririn da ta haifa tare da ba wata mata da ba a tantance ba kwana daya bayan ta haihu.

Ta ce Ukpabio ya ba ta Naira 185,000 kuma ya yi mata barazanar cewa ba za ta sake dawowa da yaron ba ko kuma ya kama ta ya karbo mata sauran yaran biyu.

Daga karshe ta kai rahoton faruwar lamarin ga wani mai fafutukar kare hakkin jama’a, Dokta Abiola Akiyode-Afolabi, wanda ya roki jami’an tsaro da su shiga cikin lamarin.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp