fidelitybank

An kori Babban hafsan ‘yan sanda bayan jita-jitar juyin mulki

Date:

Shugaban Sudan ta Kudu Salva Kiir ya kori babban hafsan ‘yan sandan kasar Laftanar Janar Majak Akec Malok daga mukaminsa, a wani mataki na hukunta jami’an tsaron bayan samun rahotannin yuƙurin yi masa juyin mulki

Shugaban ya sanar da maye gurbinsa a gidan talabijin na kasar, inda ya nada Laftanar Janar Atem Marol Biar a matsayin sabon shugaban ‘yan sanda.

A ranar 11 ga watan Nuwamba ne aka fara yada jita-jitar juyin mulkin, yayin da Shugaba Kiir ke birnin Riyadh don halartar taron Saudiyya da Afirka.

Washegari, rahotonni sun ce an kama jami’an soji da na leken asiri 27.

Ƙasar ta gabashin Afirka da ke shirin gudanar da zabenta na farko tun bayan samun ‘yancin kai a shekara ta 2011, na fuskantar sauye-sauyen tsaro da aka dade ana jira.

A halin da ake ciki kuma, kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya (MDD) ya kara wa’adin dakarun wanzar da zaman lafiya a yankin Abyei da ake takaddama a kai na tsawon shekara guda.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp