Sama da cibiyoyin kiwon lafiya dari da shagunan masu sayar da magani aka rufe a karamar hukumar Tudunwada da ke jihar Kano, ciki har da asibitin da wani likitan tiyata na jabu da ake haihuwa a asibitin.
Rufewa da kame masu gidajen ya biyo bayan rahotannin mutuwar mata da dama yayin da suke haihuwa da kuma marasa lafiya da suka samu nakasu bayan amfani da cibiyoyin kiwon lafiya.
Karamar hukumar, ta damu da ci gaban da aka samu ta kafa kwamitin lafiya karkashin jagorancin wani shugaban al’umma, Abubakar Usman Kareba wanda ya binciki lamarin tare da bankado dimbin cibiyoyin kiwon lafiya na bogi da ke aiki ba bisa ka’ida ba a yankin.
Kareba ya shaidawa manema labarai cewa bayan rufe cibiyoyin kiwon lafiya na jabu, an kama ma’aikatansu.
Ya ce karamar hukumar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen daukar tsauraran matakai na shari’a a kan duk wadanda aka kama, daga ciki akwai ma’aikacin likitancin gargajiya amma yana haihuwar mata jarirai tare da yin aikin tiyata.
Likitan na jabu, James Bawa wanda dan jihar Kaduna ne, ya amince cewa, yana da laifukan da ake tuhumarsa da shi, amma ya nemi kwamitin da ya yafe masa tare da alkawarin komawa jiharsa.
Wani mai suna Malam Shehu, mai kula da magungunan gargajiya, ya yarda cewa ya dade yana aikin tiyata a yankin, kuma yana yi wa marasa lafiya allura da karbar mata masu nakuda.
Shugaban Kwamitin, Abubakar Usman Kareba ya bada tabbacin cewa ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen daukar matakin shari’a a kan duk wadanda aka kama da nufin hana wasu.