fidelitybank

An kashe ƴan Bindiga sama da dubu 13 a mulkin Tinubu

Date:

Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa dakarun ƙasar sun kashe ‘ƴan ta’adda da masu aikata ta’asa a ƙasar sama da 13,543 a yankin arewa maso gabashin ƙasar tun bayan hawan shugaban ƙasar kan mulki kimanin shekara biyu da suka gabata.

Hakan na ƙunshe ne a cikin rahoto kan nasarorin da gwamnatin Tinubu ta samu a ɓangaren tsaro, wanda mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu ya bayar a ranar Talata.

Haka gwamnatin ƙasar ta bayyana cewa an ƙwato tare da lalata makamai sama da 11,118 a tsakankanin lokacin a yankin na ƙasar.

Ribadu ya ƙara da cewa iyalan ƴan Boko Haram da ISWAP sama da 124,408, sun miƙa wuya, sannan an ƙwato alburusai sama da 252,596.

Yankin arewa maso gabas dai ya ƙunshi jihohin Borno da Adamawa da Yobe da Bauchi da Gombe da Taraba, kuma yanki ne da ya shafe sama da shekara 10 yana fama da rikice-rikicen Boko Haram wanda ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane, tare da raba miliyoyi da muhallansu

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...
X whatsapp