fidelitybank

An kashe ‘yan sanda 6 a jihar Delta

Date:

Rundunar ‘yansandan Najeriya ta tabbatar da kashe wasu jami’anta shida a jihar Delta.

A watan Janairu ne ‘yan bindiga suka sace wasu ‘yansanda uku da ke kan aiki, lokacin da aka kira su wani waje da ake hatsaniya a Ohoro cikin Ƙaramar Hukumar Ughelli ta arewa.

Jami’an uku na cikin tawagar ‘yansada shida da aka kai wajen duba ababan hawa a Ughelli kan titin Patani.

Makonni kaɗan aka sake kai wasu ‘yansandan domin ceto abokan aikinsu da aka sace.

Yayin wannan aiki ne aka yi wa ‘yansandan kofar rago aka kashe su a wajen dajin Ohoro da ke ƙaramar hukumar Ughelli.

Cikin sanarwar da ya fitar a ranar Asabar, kakain ‘yansandan jihar Muyiwa Adejobi, ya ce an gano gawarwakin jami’an shida da aka kashe, ana kuma ci gaba da neman wasu jami’ai shida na daban.

“An gano gawar waɗannan jami’an ne lokacin da ake binciken haɗin gwiwa tsakanin ‘yansanda da sauran jami’an tsaro,” in ji Adejobi.

“Rundunarmu ta mayar da hankali wajen neman sauran jami’anmu shida, a gefe guda kuma mun tuntubi duka iyalansu kan wannan batu.

“Waɗanda suka mutu sun hada da Sifeto Abe Olubunmi da ya fara aiki 1 ga watan Agusta, 2003, Septo Friday Irorere 1 ga watan Janairun 2003, Sajan Kuden Elisha 17 ga watan oktoba 2011, Sajan Akpan Aniette shi ma 17 ga watan Oktoba 2011, Sajan Ayere Paul 17 ga Oktoba 2011, sai kuma Sajan Ejemito Friday wanda shi ma ya fara aiki 17 Oktoba 2011.

“Jami’an da ake ci gaba da nema kuma sun haɗa da Sefeto Onoja Daniel enlisted da Sefeto Onogho Felix da Sefeto Emmanuel Okoroafor enlisted da Sufeto Joel Hamidu.

“Akwai kuma Sajan Moses Eduvie da kuma Sajan Cyril Okorie,” in ji sanarwar

Ya ce za a yi bikin binne waɗannan jami’ai a Abuja ranar 5 ga watan Afrilu.

Ya zuwa yanzu an kama mutum biyar da ake zargi da hannu cikin kashe jami’an.

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...
X whatsapp