Rundunar sojoji ta ce, ta kashe ‘yan fashin daji uku tare da ceto mutum 10 da aka yi garkuwa da su a Jihar Kaduna da ke arewacin ƙasar.
Wata sanarwa ta ce dakarun sun yi nasarar kashe ‘yan bindigar ne a dajin Kabode da ke ƙaramar hukumar Chikun ranar Juma’a bayan sun yi musu kwanton-ɓauna.
Kafin haka, a ranar Alhamis kuma dakarun suka bi sawun wasu mutane da aka ce an sace a ƙauyen Danbaba na ƙaramar hukumar Igabi.
“Da ganin dakarun a Birnin Yero, sai ‘yan fashin suka gudu suka bar dukkan mutum 10 da suka yi garkuwa da su,” a cewar sanarwar da aka fitar a yau Asabar.
Ta ƙara da cewa an haɗa mutanen da iyalansu bayan likitoci sun duba lafiyarsu.