fidelitybank

An kashe ‘yan Boko Haram a Kamaru

Date:

Dakarun haɗin gwiwa da ke yaƙar Boko Haram – MNJTF ƙarƙashin rundunar ta ɗaya da ke garin Mora a Kamaru sun kashe mayaƙan Boko Haram uku a sumame daban-daban da suka kai a Zigue da Soueram a ranakun 15 da kuma 22 na watan Afrilun 2024.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar soji, Leftenar Kanar Abubakar Abdullahi ya sanyawa hannu ta ce a harin farkon na ranar 15 ya faru ne a garin Zigue da ke iyakar Kamaru wanda ya yi sanadiyyar kashe ɗan boko haram ɗaya.

Hari na biyu ya faru a safiyar ranar 22 a garin Soueram da ke kusa da iyakar Kamaru da Najeriya inda dakarun suka yi nasarar kashe wasu mayaƙan Boko Haram guda biyu.

Yayin sumamen an gano bindigar PKM guda ɗaya da AK-47 ɗaya da alburusai 5 da kuma harsasai guda 20.

Sanarwar ta ce dakarun sun ci gaba da nuna jin daɗinsu kan yadda mazauna garuruwan ke basu goyon baya da kuma samar masu da bayanai wanda ya taimaka masu wajen cimma nasarorin.

Ya ce “muna neman al’umomi su ci gaba da bamu goyon baya kuma MNJTF za ta ci gaba da tabbatar da zaman lafiya da tsaro a tafkin Chadi da ƙara ƙarfafa murƙushe ayyukan ta’addanci a yankin”.

www.nigeriannewspapers.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp