Wasu ‘yan ta’adda a jihar Bauchi sun kashe wani mutum mai suna Peter tare da raunata wani Dokagk Danladi mai shekaru 38 da haifuwa, bisa zargin satar karnuka.
An kai harin ne a daren ranar 9 ga watan Afrilu a yankin Lushi da ke jihar.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, 10 ga watan Afrilu, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi, Ahmed Wakil, ya ce, “Mutane biyun da aka kashe an zarge su ne da laifin satar kare kuma wasu fusatattun matasa sun kai musu hari da misalin karfe 11:30 na rana.
A cewar Wakil, an kashe Peter ne a wurin, yayin da Danladi ya samu raunuka da dama a kai, inda aka garzaya da shi asibitin koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa domin samun kulawar gaggawa.
Tawagar ‘yan sanda karkashin jagorancin jami’in ‘yan sandan yankin sun ziyarci wurin domin tattara shaidu da kuma bin diddigin wadanda suka kai harin.
Wakil ya tabbatar wa da jama’a cewa ana gudanar da cikakken bincike, inda ya ce, “Hukumar ba za ta bar wani abu ba wajen hukunta duk wanda ya aikata laifin.”
Da yake yin Allah wadai da harin, kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi, Sani-Omolori Aliyu, ya bayyana wannan aika-aika a matsayin “batsa” da kuma “mummunar cin fuska ga bin doka da oda.
Ya nanata cewa babu wani dan kasa da ke da hakkin daukar doka a hannunsu.
Aliyu ya kara da cewa, “Komai laifin da ake zargin, dole ne a mika wadanda ake tuhuma ga hukumomin tsaro domin bin ka’ida.
Ya kuma tabbatar wa mazauna garin cewa ‘yan sanda na ci gaba da jajircewa wajen ganin ba a sake aukuwar irin wadannan abubuwan da suka sabawa doka ba, yana mai kira ga jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da baiwa hukumomi hadin kai yayin da ake ci gaba da bincike.