fidelitybank

An kashe wani Matashi a kan faɗan Kare

Date:

Wasu ‘yan ta’adda a jihar Bauchi sun kashe wani mutum mai suna Peter tare da raunata wani Dokagk Danladi mai shekaru 38 da haifuwa, bisa zargin satar karnuka.

An kai harin ne a daren ranar 9 ga watan Afrilu a yankin Lushi da ke jihar.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin a cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, 10 ga watan Afrilu, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi, Ahmed Wakil, ya ce, “Mutane biyun da aka kashe an zarge su ne da laifin satar kare kuma wasu fusatattun matasa sun kai musu hari da misalin karfe 11:30 na rana.

A cewar Wakil, an kashe Peter ne a wurin, yayin da Danladi ya samu raunuka da dama a kai, inda aka garzaya da shi asibitin koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa domin samun kulawar gaggawa.

Tawagar ‘yan sanda karkashin jagorancin jami’in ‘yan sandan yankin sun ziyarci wurin domin tattara shaidu da kuma bin diddigin wadanda suka kai harin.

Wakil ya tabbatar wa da jama’a cewa ana gudanar da cikakken bincike, inda ya ce, “Hukumar ba za ta bar wani abu ba wajen hukunta duk wanda ya aikata laifin.”

Da yake yin Allah wadai da harin, kwamishinan ‘yan sandan jihar Bauchi, Sani-Omolori Aliyu, ya bayyana wannan aika-aika a matsayin “batsa” da kuma “mummunar cin fuska ga bin doka da oda.

Ya nanata cewa babu wani dan kasa da ke da hakkin daukar doka a hannunsu.

Aliyu ya kara da cewa, “Komai laifin da ake zargin, dole ne a mika wadanda ake tuhuma ga hukumomin tsaro domin bin ka’ida.

Ya kuma tabbatar wa mazauna garin cewa ‘yan sanda na ci gaba da jajircewa wajen ganin ba a sake aukuwar irin wadannan abubuwan da suka sabawa doka ba, yana mai kira ga jama’a da su kwantar da hankalinsu tare da baiwa hukumomi hadin kai yayin da ake ci gaba da bincike.

@nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp