fidelitybank

An kashe wani dan fashin da ya addabi Nasarawa

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Nasarawa ta ce jami’anta sun yi nasarar kashe wani da ake zargin dan fashi da makami mai suna Ifienyichukwu Ilegalu a yankin Mararaba da ke karamar hukumar Karu a wani samame na fashi da makami.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, DSP Ramhan Nansel, ya bayyana a wata sanarwa a ranar Asabar cewa an kama wani Edache Joseph, wanda ke cikin ‘yan fashin.

Ramhan Nansel ya bayyana cewa kama shi ya biyo bayan matakin da kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Umar Shehu Nadada, ya yi na yin kwaskwarima ga tsarin aikin ‘yan sanda na yankin Maraba, inda a baya-bayan nan aka samu rahotannin faruwar al’amura na fashi da makami.

Ya ce rundunar ta samu bayanai ne a ranar 5 ga watan Afrilu cewa, wasu gungun ‘yan fashi da makami 8 ne suka far wa wasu mazauna unguwar Aso pada da ke yankin Mararaba.

Sanarwar ta ce, bayan samun bayanan ne jami’an ‘yan sanda tare da hadin gwiwar ‘yan banga da wasu jajirtattun jama’ar yankin suka bi sawun ‘yan ta’addan, lamarin da ya kai ga kashe wani da ake zargin tare da kama wani.

“Wanda ake zargin ya yi bayani mai amfani, kuma yana taimaka wa ‘yan sanda wajen gudanar da bincike.

“Kwamishanan ‘yan sandan ya yabawa kokarin jami’an ‘yan sanda, kungiyar ‘yan banga, da sauran al’umma bisa bajintar da suka nuna, ya kuma ba su tabbacin ci gaba da ba su goyon baya. Ya kuma umurci sauran jama’a da su ba ‘yan sanda hadin kai domin kawar da masu aikata laifuka a jihar,” in ji sanarwar.

nnn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp