fidelitybank

An kashe sojoji a Sudan bayanƙazamin faɗa

Date:

Rahotanni sun ce ana ci gaba da gwabza kazamin faɗa a babban birnin ƙasar Sudan, Khartoum, da kuma yankin Darfur da ke yammacin ƙasar.

Rahotannin sun kuma ce an kashe ɗaruruwan mutane a faɗan da ake ci gaba da yi.

Shaidu sun bayyana wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa gawawwakin mutane sun cika kan titunan birnin Omdurman a ranar Alhamis, a wani sabon rikici da ya ɓarke tsakanin sojojin Sudan da dakarun RSF.

“Gawawwakin mutane sanye da kakin soji sun cika kan titunan tsakiyar birnin bayan faɗa a jiya,” kamar yadda wani shaida ya ruwaito.

Hukumar kula da masu ƙaura ta duniya (IOM) ta ce an kashe mutane 700 a rikici a yammacin Darfur.

An kuma ruwaito ɓacewar mutane sama da 300 bayan kazamin faɗa da aka yi a birnin El Geneina.

Shaidu sun zargi dakarun RSF da kai wa waɗanda ba larabawa hari da kuma kashe su a rikicin.

Ofishin jakadancin Amurka da ke birnin Khartoum ya ce ya damu matuka da rahotannin da shaidu suka bayar na cin zarafin bil adama da RSF da kuma wasu mayaka ke yi.

Sai dai RSF ta ce ba ta da hannu a abin da ta bayyana a matsayin “rikicin kabilanci”.

Dubban mutane ne suka tsallaka zuwa ƙasar Chadi a cikin ‘yan kwanakin da suka gabata domin samun tsira.

Kusan mutane miliyan shida ne aka tilastawa barin gidajensu tun lokacin da yaƙin ya ɓarke a tsakiyar watan Afrilu.

sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...
X whatsapp