fidelitybank

An kashe sojoji a Sudan bayanƙazamin faɗa

Date:

Rahotanni sun ce ana ci gaba da gwabza kazamin faɗa a babban birnin ƙasar Sudan, Khartoum, da kuma yankin Darfur da ke yammacin ƙasar.

Rahotannin sun kuma ce an kashe ɗaruruwan mutane a faɗan da ake ci gaba da yi.

Shaidu sun bayyana wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa gawawwakin mutane sun cika kan titunan birnin Omdurman a ranar Alhamis, a wani sabon rikici da ya ɓarke tsakanin sojojin Sudan da dakarun RSF.

“Gawawwakin mutane sanye da kakin soji sun cika kan titunan tsakiyar birnin bayan faɗa a jiya,” kamar yadda wani shaida ya ruwaito.

Hukumar kula da masu ƙaura ta duniya (IOM) ta ce an kashe mutane 700 a rikici a yammacin Darfur.

An kuma ruwaito ɓacewar mutane sama da 300 bayan kazamin faɗa da aka yi a birnin El Geneina.

Shaidu sun zargi dakarun RSF da kai wa waɗanda ba larabawa hari da kuma kashe su a rikicin.

Ofishin jakadancin Amurka da ke birnin Khartoum ya ce ya damu matuka da rahotannin da shaidu suka bayar na cin zarafin bil adama da RSF da kuma wasu mayaka ke yi.

Sai dai RSF ta ce ba ta da hannu a abin da ta bayyana a matsayin “rikicin kabilanci”.

Dubban mutane ne suka tsallaka zuwa ƙasar Chadi a cikin ‘yan kwanakin da suka gabata domin samun tsira.

Kusan mutane miliyan shida ne aka tilastawa barin gidajensu tun lokacin da yaƙin ya ɓarke a tsakiyar watan Afrilu.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp