Wasu mahara dauke da makamai sun kai wa sojoji biyu na bataliya ta 312 Barrack Kalapanzi hari a Babar Saura a jihar Kaduna.
Zagazola Makama, kwararre kan yaki da tada kayar baya da ya mayar da hankali kan yankin tafkin Chadi, ne ya bayyana hakan a wani sako da ya wallafa a hannunsa na X.
Makama ya bayyana cewa wasu majiyoyin leken asiri ne suka sanar da shi cewa wasu maharan uku dauke da manyan muggan makamai ne suka bindige sojojin, inda daya daga cikinsu mai suna Kofur James (wanda ba a san sunan sa ba) ya mutu, sannan kuma Private Ibrahim Bazalla ya jikkata.
Masanin tsaro ya bayyana cewa maharan sun sace bindigogin AK-47 guda biyu daga hannun sojojin kafin daga bisani su arce daga wurin.
Rahoton ya ce, an garzaya da wadanda harin ya rutsa da su zuwa Asibitin Reference na Sojoji 44, inda aka tabbatar da mutuwar Kofur James, yayin da Private Bazalla ke samun kulawar jinyar raunin da ya samu.
Makama ya bayyana cewa an bi sahun maharan ne zuwa Degel 2, Kaduna, inda suka yi watsi da wata mota kirar Toyota Corolla ta azurfa, bayan wani samame na hadin gwiwa da sojoji, ‘yan sanda, da kungiyoyin ‘yan banga suka yi.
“Yayin da suke yunkurin tserewa, maharan sun kwace wata farar mota kirar Toyota Venza daga hannun wani farar hula mai suna Abdullahi Mohammed, da ke Badarawa, Kaduna.
Ya kara da cewa “ana ci gaba da kokarin kama wadanda ake zargin tare da kwato motar da aka sace.”