Ƴansanda da sojoji sun yi rikici a jihar Ebonyi, wanda ya yi sanadiyar mutum ɗaya wanda ya zo wucewa.
Rikicin wanda aka yi a ranar Laraba, ya faru ne a yankin Ugwuachara bayan an samu saɓani tsakanin ƴansanda da suke duba motoci a hanya da wani soja da yake kan babur, kamar yadda tashar Channels ta ruwaito.
Wani ganau ya ce sojan ne ya ƙi amince a duba babur ɗinsa, shi kuma ɗansandan ya yi yunƙurin kama babur ɗin.
A lokacin da rikicin ne aka harbi wani mutum daban ya rasu, sannan wasu mutum uku suka jikkata.
Kwamishinar ƴansandan jihar Ebonyi, Anthonia Uche-Anya ta tabbatar da aukuwar lamarin a tattaunawarsa da tashar Channles ta wayar tarho.
Ta ce da sojan da ɗansandan duk suna hannu, kuma ana cigaba da bincike.