fidelitybank

An kashe mutum guda tare da jikkata da dama a wani rikici a Bauchi

Date:

Wata hatsaniya a kauyen Zaranda da ke karamar hukumar Toro na jihar Bauci, ta janyo mutuwar mutum ɗaya da kuma jikkata wasu da dama.

Cikin wata sanawar da mai magana da yawun ƴansandan jihar, Ahmed Wakili ya fitar, ta ce an jikkata mutum uku daga garin Zaranda a rikicin.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9 na safiyar Talata, lokacin da mazauna garin suka fito domin nuna fushi kan wani mai sayar da gawayi da aka kama, kamar yadda rahotonni suka ruwaito.

Zanga-zangar da suka fito domin nuna ɓacin-ransu ta kuma saka ƙungiyar maharba da tabbatar da tsaro harba bindigogi a sama.

Wakili ya ce an garzaya da su zuwa cibiyar kiwon lafiya a garin, inda Allah ya yi wa ɗaya daga cikinsu mai suna Yahaya cikawa.

Kwamishinan ƴansanda a jihar, Auwal Muhammad, ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan mutuwar Yahaya da kuma abin da wasu jami’an tsaro da ke cikin lamarin suka aikata.

“Tuni muka ɗauki mataki domin shawo kan lamarin da gudanar da bincike, sannan mu gabatar da waɗanda suka aikata wannan abu,” in ji sanarwar ƴansandan.

Sanarwar ta kuma ce an aika tawagar jami’an tsaro zuwa wurin da lamarin ya faru domin mayar da doka da oda da kuma sake buɗe hanyar da mazauna garin suka toshe.

legit news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp