An tabbatar da mutuwar mutum daya tare da kona shaguna da dama bayan wani kazamin rikici da ya barke tsakanin matasa daga kauyukan Faruruwa da Tarandai a karamar hukumar Takai a jihar Kano.
Lamarin, wanda ya faru da misalin karfe 7:45 na dare. A ranar 23 ga watan Mayu yayin wata kasuwa a Faruruwa, wani manazarci kan harkokin tsaro Zagazola Makama ne ya bayyana hakan a wani sakon da ya fitar ta hanyar tabbatar da sahihancin sa a ranar Lahadi.
A cewar Makama, rikicin ya samo asali ne bayan wani matashi mai shekaru 28 mai suna Sani Yunusa da ke kauyen Toho Diribo ya ziyarci budurwarsa a garin Tarandai.
Rahotanni sun bayyana cewa wasu matasa da ake zargin ‘yan kauye ne suka yi masa kwanton bauna a hanyarsa ta dawowa, inda suka kai masa hari da sanduna da yankan katako.
“Rikicin ya kai ga kone shaguna da dama a cikin kasuwar,” in ji sanarwar.
An baza jami’an tsaro cikin gaggawa zuwa yankin domin kwantar da hankula tare da hana barkewar rikici.
Majiyar ‘yan sandan ta tabbatar da cewa al’amura sun dawo daidai amma sun tabbatar da cewa ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano musabbabin rikicin tare da gurfanar da wadanda suka aikata wannan aika-aika a gaban kuliya.