fidelitybank

An kashe Mutum guda a wani rikici a Kano

Date:

An tabbatar da mutuwar mutum daya tare da kona shaguna da dama bayan wani kazamin rikici da ya barke tsakanin matasa daga kauyukan Faruruwa da Tarandai a karamar hukumar Takai a jihar Kano.

Lamarin, wanda ya faru da misalin karfe 7:45 na dare. A ranar 23 ga watan Mayu yayin wata kasuwa a Faruruwa, wani manazarci kan harkokin tsaro Zagazola Makama ne ya bayyana hakan a wani sakon da ya fitar ta hanyar tabbatar da sahihancin sa a ranar Lahadi.

A cewar Makama, rikicin ya samo asali ne bayan wani matashi mai shekaru 28 mai suna Sani Yunusa da ke kauyen Toho Diribo ya ziyarci budurwarsa a garin Tarandai.

Rahotanni sun bayyana cewa wasu matasa da ake zargin ‘yan kauye ne suka yi masa kwanton bauna a hanyarsa ta dawowa, inda suka kai masa hari da sanduna da yankan katako.

“Rikicin ya kai ga kone shaguna da dama a cikin kasuwar,” in ji sanarwar.

An baza jami’an tsaro cikin gaggawa zuwa yankin domin kwantar da hankula tare da hana barkewar rikici.

Majiyar ‘yan sandan ta tabbatar da cewa al’amura sun dawo daidai amma sun tabbatar da cewa ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano musabbabin rikicin tare da gurfanar da wadanda suka aikata wannan aika-aika a gaban kuliya.

latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ministan harkokin jin Æ™ai ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na Æ™asa

Ministan harkokin jin kai, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya zama...

Amurka za ta lalata magungunan takarar haihuwa na dala miliyan 10 da za a kawo Afrika

Gwamnatin Amurka na shirin lalata magungunan tazarar haihuwa da...

Hukumar NAFDAC ta kama abubuwan fashewa a Kano

A cewar hukumar, an gano lita 60,000 na sulphuric...

Sojoji sun fafata da da ‘yan Bindiga a Neja

Rundunar sojiji ta ce, sojoji tare da haÉ—in gwiwar...

Majalisar Dinkin Duniya za ta dakatar da tallafin abinci a Najeriya

Shirin Abinci na Majalisar ÆŠinkin Duniya (WFP) ya bayyana...

Tinubu ya na murkushe ‘Yan adawa – Sule Lamido

Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya ce...

Gwamnatin Kano ta baiwa yara fifiko – UNICEF

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya...

Majalisar ta amince da buƙatar Tinubu na ciyo bashin dala biliyan 21

A ranar Talata ne majalisar Dattawa ta amince da...

An sallami Gwamnan Katsina daga asibiti bayan ya samu rauni a hatsarin mota

An sallami gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda,...

Har yanzu Tinubu bai nada Jakadun Najeriya ba – ADC

Jam’iyyar ADC ta soki yadda gwamnatin APC ta shugaba...

Har yanzu ina LP kuma ni ne zan iya saita Najeriya – Datti

Datti Baba-Ahmed, tsohon dan takarar mataimakin shugaban kasa a...

APC ta zama buhun kusa ta gaza a Najeriya – Amaechi

Tsohon gwamnan jihar Ribas, Chibuike Amaechi ya bayyana jam'iyyar...
X whatsapp