fidelitybank

An kashe mutane huɗu tare da sace mataimakin shugaban ƙaramar hukuma a Zamfara

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun kashe mutane hudu tare da yin garkuwa da mataimakin shugaban karamar hukumar Bukkuyyum a jihar Zamfara, Hon. Bala Muhammad Maijidadi da wasu da dama a yankin.

Rahotanni na cewa an kai hare-haren hadin gwiwa tsakanin daren Lahadi zuwa safiyar Litinin.

Wani magidanci mai suna Nasiru Adamu ya shaidawa manema labarai ta wayar tarho a daren ranar Talata cewa ‘yan bindigar sun kai farmaki unguwar Shemori dake gundumar Mada Gusau da misalin karfe 9:20 na daren Lahadi inda suka yi garkuwa da wasu mata shida.

An kuma tattaro cewa da sanyin safiyar ranar Litinin ne wasu gungun ‘yan bindiga suka kai hari a kauyen Kairu da ke gundumar Zugu, inda suka kashe wasu mutanen yankin biyu tare da yin awon gaba da wasu mutanen da ba a tantance adadinsu ba.

A garin Mada da ke gundumar Gusau, ‘yan bindigar sun far wa Hayin Bajumi, inda suka kona gidan wani Aliyu Usman.

“Gobarar ta kashe ‘ya’yansa biyu, Ishaq Aliyu mai shekaru biyar da Jafar Aliyu mai shekaru biyu.

“’Yan bindigar sun kuma yi awon gaba da matar makwabcin Usman, tare da jaririnta mai shekara daya kafin su gudu daga wurin,” majiyar ta bayyana.

Duk kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Yazeed Abubakar ya ci tura har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

daily post today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp