fidelitybank

An kashe mutane huɗu tare da sace mataimakin shugaban ƙaramar hukuma a Zamfara

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun kashe mutane hudu tare da yin garkuwa da mataimakin shugaban karamar hukumar Bukkuyyum a jihar Zamfara, Hon. Bala Muhammad Maijidadi da wasu da dama a yankin.

Rahotanni na cewa an kai hare-haren hadin gwiwa tsakanin daren Lahadi zuwa safiyar Litinin.

Wani magidanci mai suna Nasiru Adamu ya shaidawa manema labarai ta wayar tarho a daren ranar Talata cewa ‘yan bindigar sun kai farmaki unguwar Shemori dake gundumar Mada Gusau da misalin karfe 9:20 na daren Lahadi inda suka yi garkuwa da wasu mata shida.

An kuma tattaro cewa da sanyin safiyar ranar Litinin ne wasu gungun ‘yan bindiga suka kai hari a kauyen Kairu da ke gundumar Zugu, inda suka kashe wasu mutanen yankin biyu tare da yin awon gaba da wasu mutanen da ba a tantance adadinsu ba.

A garin Mada da ke gundumar Gusau, ‘yan bindigar sun far wa Hayin Bajumi, inda suka kona gidan wani Aliyu Usman.

“Gobarar ta kashe ‘ya’yansa biyu, Ishaq Aliyu mai shekaru biyar da Jafar Aliyu mai shekaru biyu.

“’Yan bindigar sun kuma yi awon gaba da matar makwabcin Usman, tare da jaririnta mai shekara daya kafin su gudu daga wurin,” majiyar ta bayyana.

Duk kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Yazeed Abubakar ya ci tura har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

legit.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...
X whatsapp