fidelitybank

An kashe mutane huɗu tare da sace mataimakin shugaban ƙaramar hukuma a Zamfara

Date:

Wasu ‘yan bindiga sun kashe mutane hudu tare da yin garkuwa da mataimakin shugaban karamar hukumar Bukkuyyum a jihar Zamfara, Hon. Bala Muhammad Maijidadi da wasu da dama a yankin.

Rahotanni na cewa an kai hare-haren hadin gwiwa tsakanin daren Lahadi zuwa safiyar Litinin.

Wani magidanci mai suna Nasiru Adamu ya shaidawa manema labarai ta wayar tarho a daren ranar Talata cewa ‘yan bindigar sun kai farmaki unguwar Shemori dake gundumar Mada Gusau da misalin karfe 9:20 na daren Lahadi inda suka yi garkuwa da wasu mata shida.

An kuma tattaro cewa da sanyin safiyar ranar Litinin ne wasu gungun ‘yan bindiga suka kai hari a kauyen Kairu da ke gundumar Zugu, inda suka kashe wasu mutanen yankin biyu tare da yin awon gaba da wasu mutanen da ba a tantance adadinsu ba.

A garin Mada da ke gundumar Gusau, ‘yan bindigar sun far wa Hayin Bajumi, inda suka kona gidan wani Aliyu Usman.

“Gobarar ta kashe ‘ya’yansa biyu, Ishaq Aliyu mai shekaru biyar da Jafar Aliyu mai shekaru biyu.

“’Yan bindigar sun kuma yi awon gaba da matar makwabcin Usman, tare da jaririnta mai shekara daya kafin su gudu daga wurin,” majiyar ta bayyana.

Duk kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Yazeed Abubakar ya ci tura har zuwa lokacin hada wannan rahoto.

legitnewsnigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp