fidelitybank

An kashe mutane akalla 117, an sace wasu 130 sannan sama da 10,463 suka rasa cikin kwana 4 a Kaduna

Date:

Majalisar wakilai a ranar Alhamis, ta bukaci gwamnatin tarayya da ta umurci sufeto janar na ‘yan sandan Najeriya, Usman Baba, da ya tura tawagar tsaro ta musamman a yankin Birnin Gwari da Giwa na jihar Kaduna, domin magance ‘yan ta’adda da ke addabar yankin.

Majalisar ta kuma bukaci babban hafsan sojin kasa, Laftanar Janar, Faruk Yahaya, da babban hafsan sojin sama, Air Marshal Isiaka Oladayo Amao, da su kara kaimi wajen yaki da ‘yan ta’adda da ‘yan fashi a kasar nan.

Kudurin ya biyo bayan wata muhawara kan kudirin gaggawa na magance yawaitar hare-haren ‘yan bindiga, garkuwa da mutane da kashe-kashe a fadin kananan hukumomin Birnin Gwari da Giwa na jihar da dan majalisa mai wakiltar yankin, Shehu Balarabe ya yi.

Balarabe, a zauren majalisar, ya ce, an kashe mutane akalla 117, an sace wasu 130 sannan sama da 10,463 suka rasa matsugunansu a kananan hukumomin biyu tsakanin ranakun 24 zuwa 28 ga Maris.

Dan majalisar ya ce, an yi awon gaba da shanu marasa adadi yayin da aka kona gidaje da wasu kayayyaki masu daraja a lokacin da ‘yan bindigar suka kai wa mazabar sa hari.

Ya kuma bukaci gwamnatin tarayya da ta samar da sansanonin ‘yan gudun hijira da kuma samar da kayan agaji, domin tallafawa wadanda hare-haren ya rutsa da su.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...
X whatsapp