Majalisar wakilai a ranar Alhamis, ta bukaci gwamnatin tarayya da ta umurci sufeto janar na ‘yan sandan Najeriya, Usman Baba, da ya tura tawagar tsaro ta musamman a yankin Birnin Gwari da Giwa na jihar Kaduna, domin magance ‘yan ta’adda da ke addabar yankin.
Majalisar ta kuma bukaci babban hafsan sojin kasa, Laftanar Janar, Faruk Yahaya, da babban hafsan sojin sama, Air Marshal Isiaka Oladayo Amao, da su kara kaimi wajen yaki da ‘yan ta’adda da ‘yan fashi a kasar nan.
Kudurin ya biyo bayan wata muhawara kan kudirin gaggawa na magance yawaitar hare-haren ‘yan bindiga, garkuwa da mutane da kashe-kashe a fadin kananan hukumomin Birnin Gwari da Giwa na jihar da dan majalisa mai wakiltar yankin, Shehu Balarabe ya yi.
Balarabe, a zauren majalisar, ya ce, an kashe mutane akalla 117, an sace wasu 130 sannan sama da 10,463 suka rasa matsugunansu a kananan hukumomin biyu tsakanin ranakun 24 zuwa 28 ga Maris.
Dan majalisar ya ce, an yi awon gaba da shanu marasa adadi yayin da aka kona gidaje da wasu kayayyaki masu daraja a lokacin da ‘yan bindigar suka kai wa mazabar sa hari.
Ya kuma bukaci gwamnatin tarayya da ta samar da sansanonin ‘yan gudun hijira da kuma samar da kayan agaji, domin tallafawa wadanda hare-haren ya rutsa da su.