Kimanin mutane tara (9) ne wasu da ake zargin Fulani ne suka kashe a kauyukan Ruji da Atakjeh na masarautar Atyap da ke karamar hukumar Zangon Kataf a jihar Kaduna.
Rahotanni sun bayyana cewa, an kashe wani matashi a kauyen Ruji, yayin da kuma aka kashe mutane takwas a kauyen Atakjeh a daren Laraba.
An garzaya da wasu mutane uku da suka jikkata zuwa asibiti domin yi musu magani.
Ku tuna cewa, wani kauye da ke kusa da Zangon Urban, Unguwan Wakili an kai hari tare da kashe mutane kusan 17 da wasu da ake zargin Fulani ne a masarautar Atyap kwanan nan.
Shugaban kungiyar ci gaban al’umma ta Atyap (ACDA), Dr Samuel Achi ya shaidawa DAILY POST cewa, a halin yanzu al’amura sun tabarbare a kauyen Atakjeh.
Samuel ya ce, “Abin mamaki akwai jami’an tsaro kusa da kauyen da aka kashe mutane takwas, amma sun kasa kubutar da mutanen kauyen daga hannun maharan.
“Maharan sun je kauyen ne suka gudanar da aikinsu kuma suka tafi ba tare da wani shiga tsakani daga jami’an tsaro ba.”
“Kamar yadda nake magana da ku, daya bai tabbatar da adadin wadanda aka kashe da wadanda suka jikkata ba amma a halin yanzu, muna da mutum takwas da aka kashe tare da jikkata wasu uku a kauyen Atakjeh.
“Wadanda suka samu raunuka daban-daban an kai su asibiti domin yi musu magani,” in ji shi