fidelitybank

An kashe mutane 9 a jihar Kaduna

Date:

Kimanin mutane tara (9) ne wasu da ake zargin Fulani ne suka kashe a kauyukan Ruji da Atakjeh na masarautar Atyap da ke karamar hukumar Zangon Kataf a jihar Kaduna.

Rahotanni sun bayyana cewa, an kashe wani matashi a kauyen Ruji, yayin da kuma aka kashe mutane takwas a kauyen Atakjeh a daren Laraba.

An garzaya da wasu mutane uku da suka jikkata zuwa asibiti domin yi musu magani.

Ku tuna cewa, wani kauye da ke kusa da Zangon Urban, Unguwan Wakili an kai hari tare da kashe mutane kusan 17 da wasu da ake zargin Fulani ne a masarautar Atyap kwanan nan.

Shugaban kungiyar ci gaban al’umma ta Atyap (ACDA), Dr Samuel Achi ya shaidawa DAILY POST cewa, a halin yanzu al’amura sun tabarbare a kauyen Atakjeh.

Samuel ya ce, “Abin mamaki akwai jami’an tsaro kusa da kauyen da aka kashe mutane takwas, amma sun kasa kubutar da mutanen kauyen daga hannun maharan.

“Maharan sun je kauyen ne suka gudanar da aikinsu kuma suka tafi ba tare da wani shiga tsakani daga jami’an tsaro ba.”

“Kamar yadda nake magana da ku, daya bai tabbatar da adadin wadanda aka kashe da wadanda suka jikkata ba amma a halin yanzu, muna da mutum takwas da aka kashe tare da jikkata wasu uku a kauyen Atakjeh.

“Wadanda suka samu raunuka daban-daban an kai su asibiti domin yi musu magani,” in ji shi

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...
X whatsapp