fidelitybank

An kashe mutane 46 ciki harda ɗan shugaban ƙaramar hukuma a Benue

Date:

An kashe mutane da dama a wani kazamin hari da wasu da ake zargin makiyaya ne suka kai kan al’ummar Umogidi da ke gundumar Entekpa Adoka a karamar hukumar Otukpo ta jihar Benue.

Mmmunan lamarin da ya faru a ranar Laraba ya yi sanadiyar mutuwar mutane 46 ciki har da dan shugaban karamar hukumar Otukpo, Hon. Bako Eji.

Laftanal Kanal Paul Hemba (mai ritaya), mai ba gwamna shawara na musamman kan harkokin tsaro Samuel Ortom ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Alhamis.

Ya ce, duk da cewa an gano gawarwakin mutane 46, akwai yiyuwar alkaluman wadanda suka mutu ya karu, saboda munanan raunukan da dimbin mazauna garin suka samu yayin harin.

Karanta Wannan: Da Ɗumi-Ɗumi: Ƴan Bindiga sun yi garkuwa da tsohon mataimakin Gwamnan Nasarawa

Ya ce, “Ina tabbatar muku da cewa an kai hari a Umogidi, kuma ya zuwa safiyar yau, adadin wadanda suka mutu daga wadanda aka ga a zahiri daga abin da aka ce min sun kai 46. Amma kila adadin ya fi haka saboda wasu mutane. har yanzu an ba da rahoton bacewar su.”

Sabon harin ya zo ne kwana guda bayan da ‘yan ta’addan suka mamaye al’umma tare da kashe mutane uku a ranar Talata.

Kafin faruwar lamarin, maharan sun kuma kai hari kan al’ummar Igbobi da ke karamar hukumar Apa makwabciyarta a ranar Litinin. In ji Daily Post.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...

Barau ya jagorancin gangamin zaben cike gurbi a Kano

Barau ya samu rakiyar Karamin Ministan Gidaje da Raya...

Gwamnatin Kano ta kara fadada shirin matasa 

Gwamna Abba Kabir Yusuf na Jihar Kano ya sake,...

An kaiwa Malamin addini hari a Kano bayan an jikatasu da Matarsa

Wani malamin addinin Musulunci, Malam Kabir Idris, da matarsa...

Kotun Kano ta daure wata Mata da ake zargin ta tsafe su

Kotun Majistiri mai lamba 7 da ke Nomansland, ƙarƙashin...

Dalibi ya kashe kansa a cikin Jami’a

Hukumar jami'ar Obafemi Awolowo da ke jihar Osun, sun...

Gobara na cigaba da lakume wasu yankunan Turai

Gobarar daji na ci gaba da ruruwa a sassan...

An kama Fursunoni 7 da suka tsere daga gidan kurkukun jihar Nasarawa

Hukumar kula da gidajen yari a Najeriya ta ce...
X whatsapp