fidelitybank

An kashe mutane 4 ciki har da jami’an tsaro a rikicin siyasar Rivers

Date:

An kashe aƙalla mutum biyu a jihar Ribas, lokacin da wasu matasa suka mamaye gine-gine hedikwatar ƙananan hukumomi da dama, bayan da wa’adin shugabannin ƙananan hukumomin jihar 23 ya ƙare.

Lamarin ya faru ne a jiya Talata, bayan da gwamnan jihar, Siminialayi Fubara, ya umarci shugabannin sassan mulki na ƙananan hukumomin su karɓi ragamar tafiyar da ƙananan hukumomin.

Tun a ranar Litinin aka shiga zaman ɗar-dar bayan da wasu daga cikin shugabannin ƙananan hukumomin suka lashi takobin ci gaba da zama a ofis, bisa dalilin cewa ƴan majalisar dokokin jihar 27 da ke rikici da gwamnan, waɗanda suke biyayya ga Wike sun yi wa dokar wa’adinsu kwaskwarima, ta yadda za su ci gaba da zama a muƙamansu har wata shida bayan wa’adinsu.

Duk da cewa babbar kotun jihar ta yi gyara a kan dokar, wasu daga cikin shugabannin sun lashi takobin ci gaba da zama a kan shugabancin lamarin da ya haifar da rikicin.

Da yake mayar da martani kan lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutanen, daya daga cikin manyan dattawan jihar, Chief Edwin Clark, ya ɗora alhakin rikicin a kan tsohon gwamnan jihar kuma ministan Abuja a yanzu Nyesom Wike, yana mai cewa dole ne a daina siyasar ubangida a jihar ta Ribas.

Jaridar Vanguard wadda ta ruwaito labarin ta tabbatar da kisan wani ɗansanda da kuma wani ɗansakai na ƙungiyar ƴansintiri.

Haka ita ma rundunar ƴansanda ta jihar ta tabbatar da mutuwar mutum biyu sakamakon rikicin da aka gwabza tsakanin magoya bayan gwamnan da kuma tsohon ubangidan gwamnan na siyasa wato ministan na Abuja.

tribune

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp