fidelitybank

An kashe mutane 3 yayin fashin banki a Abuja

Date:

An kashe mutum uku a wani kokarin hadin gwiwa da ‘yan sanda da sojoji suka yi na dakile wani fashin banki a unguwar Abaji da ke Abuja a ranar Alhamis.

Wata sanarwa da ta samu sa hannun jami’ar hulɗa da jama’a ta rundunar ƴan sanda a birnin Abuja, SP Josephine Adeh ta fitar ranar Juma’a, ta ce rundunar ‘yan sandan babban birnin tarayya ta samu rahoton yunƙurin fashin ne da misalin karfe biyar na yamma.

Sanarwar ta ce jami’an ƴansanda tare da haɗin gwiwar sojoji sun garzaya wurin da lamarin ya faru inda suka daƙile harin da aka kai a lokaci.

Jami’an tsaron sun yi musayar wuta da ƴan fashin inda suka yi nasarar kama mutum uku da ake zargi.

Daga cikin wadanda suka jikkata har da ɗan sanda ɗaya da kuma shugaban ƴan fashin, dukkansu an kai su asibiti amma daga baya aka tabbatar da mutuwarsu.

Sauran wadanda suka jikkata na ci gaba da samun kulawa a asibiti.

Sanarwar ta ƙara da cewa ana ci gaba da gudanar da bincike domin kamo sauran waɗanda ake zargi, waɗanda suka gudu da raunuka sanadiyyar harbin bindiga.

tribune news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp