Rahotanni sun ce an kashe manoma biyu a wani sabon hari da aka kai a unguwar Ikyungwa Tombo, kusa da al’ummar Ayilamo a karamar hukumar Logo a jihar Benue.
Aminiya ta tattaro cewa, lamarin ya faru ne a ranar Litinin da karfe 5 na yamma yayin da su biyun ke dawowa daga gonakin su.
An bayyana sunayen wadanda suka mutun a matsayin Bem Uhembe da Mungwa Zuzu, dukkansu ‘yan kauyen Tse Ibor ne da ke komawa garin Ayilamo bayan sun yi aikin gonakinsu, saboda zargin wasu da ake zargin makiyaya ne suka kwace matsugunan su.
Mutanen yankin sun ci gaba da cewa an ajiye gawarwakin wadanda suka mutu a dakin ajiye gawa na Ayilamo.
Shugaban karamar hukumar, Aber Terse, ya tabbatar wa wakilinmu ta wayar tarho cewa, wadanda suka mutu – wata mace da namiji – an yi musu dirar mikiya tare da kashe su bayan sun bar gonakinsu da yammacin ranar Litinin.
Aber ya zargi makiyayan da laifin kisan mutanen biyu sakamakon mamayar unguwar Tombo, wani wurin noma, wanda wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton makiyaya ne ke ci gaba da kai musu hari tun a shekarar 2016.