fidelitybank

An kashe makiyaya 10,000 cikin shekara 7 a kasar nan – Miyetti Allah

Date:

Ƙungiyar kare al’adun Fulani a Najeriya ta Miyetti Allah ta ce an kashe makiyaya aƙalla 10,000 tare da raba wasu miliyan biyu da muhallansu a faɗin ƙasar cikin shekara bakwai da suka wuce.

Bayanan sun fito ne bayan wani taro kan tsaro da ƙungiyar ta shirya tare da haɗin gwiwar ƙungiyar Northern Consensus Movement (NCM) ta ‘yan Arewa sakamakon matsalolin tsaro da suka ce Fulani na fuskanta, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito ranar Asabar.

Cikin wata sanarwar bayan taro a ranar Juma’a, ƙungiyar ta ce daga 2015 zuwa yanzu makiyaya da dama sun fuskanci matsaloli, inda aka sace ko kashe dabbobi fiye da miliyan huɗu.

“Yi wa Fulani baƙin fenti da nuna musu tsana da kuma rura wutar ƙabilanci a kan su da kafofin yaɗa labarai ke yi ka iya kaiwa ga kisan ƙare-dangi,” in ji sanarwar.

“Ayyukan ƙungiyoyin Indigenous People of Biafra (IPOB)/Eastern Security Network (ESN) da ’Yan-Sa-Kai sun ƙara ta’azzara lamarin da kuma kawo barazana ga zaman Najeriya ƙasa ɗaya.”

Ana yawan zargin wasu ‘yan ƙabilar Fulani da aikata fashi da garkuwa da mutane musamman a jihohin arewa maso yammacin Najeriya, abin da shugabanni da ƙungiyoyin ƙabilar ke musantawa.

legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp