Gwamnatin Jihar Yobe ta ce, mayakan kungiyar Boko Haram sun kashe dalibai 167 da malamai 3 a jihar.
Mataimakin gwamnan Yobe, Idi Barde Gubana, kuma shugaban kwamitin tattara kudade, domin tallafawa ilimi ne ya sanar da hakan cewa, gwamnatin Yobe ta saka dokar ta baci a bangaren ilimi domin farfado da ilimin.
Gwamnatin Jihar Yobe ta ce, hare-haren ‘yan ta’addar kungiyar Boko Haram ya yi sanadin mutuwar dalibai 167 da malamai uku a jihar kamar yadda Daily Trust ta rawaito.
Wasu daliban 86 da malamai biyu sun samu munanan rauni, sakamakon hare-haren da yan ta’addan suka kai musu a yunkurinsu na kawo karshen karatun boko a jihar.