fidelitybank

An kashe Buharin Yadi wanda ya addabi yankin Kaduna

Date:

Sojojin kasar nan sun kashe wani dan ta’adda mai suna Buharin Yadi, daya daga cikin manyan ‘yan bindiga da ake zargin suna ta’addanci a Arewacin kasar nan cikin shekaru goma da suka gabata.

Kwamishinan Ma’aikatar Tsaro da Harkokin Cikin Gida ta Jihar Kaduna, Samuel Aruwan, ya bayyana hakan a yau Alhamis, cewa dakarun rundunar na ‘Operation Whirl Punch’, sun yi ruwan wuta a sansanin wanda ya yi sanadiyar hallaka Buhari Alhaji Halidu wanda aka fi sani da Buharin Yadi tare da ‘yan tawagarsa.

A cewarsa, an kawo karshen Buharin Yadi da tawagarsa wanda ke da alaka da sauran kungiyoyin ta’addanci da ke kashe mutane a Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma.

A wani samame na daban kuma, dakarun sojin Najeriyar tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro sun yi nasarar fatattakar ‘yan bindiga da maɓoyar ‘yan ta’adda a kusa da Irele da Igbobini da kuma Segbemi Kiribo a yankin dajin Ese-Odo a karamar hukumar Irele ta jihar Ondo.

A yayin aikin share fagen, sojojin sun kwato bindigogi da makamai da dama.

 

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp