fidelitybank

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Date:

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan nan ya nuna cewa, cikin shekaru biyu da gwamnatin Tinubu ta hau mulki, an kashe aƙalla mutum 10,217 a hare-haren da ‘yan bindiga suka kai a jihohi daban-daban.

Jihohin sun haɗa da Benue da Edo da Katsina da Kebbi da Plateau da Sokoto da Zamfara.

Jihar Benue ce ke da mafi yawan adadin mutanen da aka kashe – inda ya kai har mutum 6,896, sai Jihar Plateau da mutum 2,630.

Amnesty International, wadda ta fitar da wannan rahoto a cikar shekaru biyu na shugaban Najeriya, Bola Tinubu kan ƙaragar mulki ta zargi gwamnatinsa da gazawa wajen kare rayukan ‘yan kasa da kuma gurfanar da waɗanda ke da hannu a aikata laifuka duk da alkawurran da gwamnatin ta sha yi na inganta tsaro.

Rahoton ya kuma bayyana cewa “an raba ɗaruruwan ƙauyuka da muhallansu musamman a Zamfara da Benue da Plateau, inda dubban mutane suka rasa matsugunansu.”

“Hare-haren sun kuma lalata ababen more rayuwa da suka haɗa da rijiyoyin burtsatse da makarantu da asibitoci wanda hakan ya kara tsananta halin da jama’a ke ciki.” rahoton ya ƙara da cewa.

Amnesty International ta gargadi cewa korar manoma daga gidajensu na kara haddasa yunwa da talauci.

A jihar Plateau, an bayyana cewa mutum 65,000 ne suka rasa matsugunansu, a Benue kuwa adadin ya kai 450,000.

“Sababbin ƙungiyoyin ‘yan bindiga da suka hada da Lakurawa a jihohin Sokoto da Kebbi, da Mamuda a Kwara, na kara tsananta rikici.” in ji rahoton

Ƙungiyar ta buƙaci gwamnati da ta dauki matakan gaggawa domin dakile irin waɗannan hare-hare da kisan gilla, tana mai cewa “lokaci na kurewa, yayin da hare-haren ‘yan bindiga da masu tayar da kayar baya ke kara tsananta.”

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp