fidelitybank

An kashe ɗan Sanda tare da ɗauke bindigarsa a Legas

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Legas a ranar Litinin, ta tabbatar da kisan wani dan sanda a yankin Ikorodu da ke jihar Legas da wasu da ba a san ko su wanene ba suka yi.

Maharan sun tsere da bindigar dan sandan da aka kashe.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Legas, SP Benjamin Hundeyin, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na ƙasa NAN cewa, wasu ‘yan sanda uku sun samu munanan raunuka a harin.

Jami’an rundunar ‘yan sanda reshen Imota da ke yankin Ikorodu suna aikin sintiri ne a lokacin da maharan suka kai hari a mahadar Emuren da ke kan titin Itokin a yankin.

Majiyoyin cikin gida sun ce maharan wadanda ake zargin ’yan fashi ne, sun yi wa tawagar ‘yan sandan kwanton bauna, inda suka bude wuta tare da kashe daya a nan take suka tsere da bindigarsa.

“A ranar Asabar ‘yan sanda sun kai farmaki maboyar ‘yan kungiyar asiri a Emuren, karamar hukumar Shagamu ta Ogun,” inji wani mazaunin garin.

NAN ta ruwaito cewa, mutane da dama da ba su ji ba ba su gani ba sun fada cikin hare-haren bindiga da jami’an ‘yan fashin suka kai a Ikorodu da kewaye a baya.

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp