fidelitybank

An kashe ƴan Bindiga sama da dubu 13 a mulkin Tinubu

Date:

Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa dakarun ƙasar sun kashe ‘ƴan ta’adda da masu aikata ta’asa a ƙasar sama da 13,543 a yankin arewa maso gabashin ƙasar tun bayan hawan shugaban ƙasar kan mulki kimanin shekara biyu da suka gabata.

Hakan na ƙunshe ne a cikin rahoto kan nasarorin da gwamnatin Tinubu ta samu a ɓangaren tsaro, wanda mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu ya bayar a ranar Talata.

Haka gwamnatin ƙasar ta bayyana cewa an ƙwato tare da lalata makamai sama da 11,118 a tsakankanin lokacin a yankin na ƙasar.

Ribadu ya ƙara da cewa iyalan ƴan Boko Haram da ISWAP sama da 124,408, sun miƙa wuya, sannan an ƙwato alburusai sama da 252,596.

Yankin arewa maso gabas dai ya ƙunshi jihohin Borno da Adamawa da Yobe da Bauchi da Gombe da Taraba, kuma yanki ne da ya shafe sama da shekara 10 yana fama da rikice-rikicen Boko Haram wanda ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane, tare da raba miliyoyi da muhallansu

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp