Akalla mutane 22 ne aka kashe a karamar hukumar Danmusa ta jihar Katsina a lokacin da wasu ‘yan bindiga suka kai wa ‘yan kasuwa hari a kan hanyarsu ta zuwa kasuwar Yantumaki.
Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Katsina sun yi artabu da ‘yan bindigar da suka yi sanadin mutuwar mutane 22.
Yayin da ‘yan bindigar suka kashe mutanen kauyen shida, jami’an tsaro sun kashe ‘yan bindiga kusan 26 a yayin harbin.
Kwamishinan tsaro na cikin gida da harkokin cikin gida, Dr Nasiru Muazu-Danmusa ya tabbatar wa NAN haka a ranar Asabar.
“Mun yi Allah wadai da abin da ya faru a karamar hukumar Danmusa inda ‘yan fashin suka far wa ‘yan kasuwa a hanyarsu ta zuwa kasuwar Yantumaki daga Maidabino.
“Sun yi wa ‘yan kasuwar kwanton bauna, inda suka kashe akalla mutane shida tare da raunata wasu, ciki har da jami’an tsaro biyu da ke rakiyar ‘yan kasuwar.
“An tattaro cewa a kalla 16 daga cikin ‘yan ta’addan ne jami’an tsaro suka kashe a wurin a yayin arangamar kuma da yawa sun tsere da raunukan harbin bindiga,” in ji shi.
Kwamishinan, ya yi ikirarin cewa an samu gagarumin ci gaba a yaki da satar shanu, fashi da makami, garkuwa da mutane da sauran miyagun laifuka a jihar tun bayan hawan gwamnatin Gwamna Dikko Radda.
“A yanzu an rage matsalar zuwa kusan kashi 60 bisa 100 daga sahihan bayanan da muke samu a fadin jihar.
“Don haka ne ‘yan ta’addan suka koma amfani da wasu hanyoyi wajen ci gaba da munanan ayyukansu,” in ji shi.