fidelitybank

An kashe ƙasurgumin ɗan Bindiga Dogo Saleh a Abuja

Date:

Rundunar ƴansandan birnin Tarayya Abuja ta sanar da kashe wani ƙasurgumin ɗanbindiga mai garkuwa da mutane, Dogo Saleh da ya birnin.

Kakakin rundunar ƴansandan birnin, SP Josephine Adeh ta shaida wa BBC cewa ɗanbindigar tare da yaransa sun addabi wasu sassan birnin Abuja, inda suke ayyukan garkuwa da mutane.

Ta ƙara da cewa sakamakon bayanan sirri da suka samu kan maɓoyar ɗanbindigar ya sa suka tura jami’ai maɓoyar domin kama shi.

”Sai dai sakamakon gumurzun harbe-harbe da jami’anmu, mun samu nasarar kashe ɗanbindigar da wasu yaransa ”, in ji kakakin ƴansandan birnin.

Ta kara da cewa ɗanbindigar – wanda shi ne babban mataimakin shugaban ƴanbidigar – ya yi ƙaurin suna wajen ayyukan ta’addanci a kan titin Abuja zuwa Kaduna.

SP Adeh ta ce a lokacin gumurzun jami’an ƴansanda sun kuɓutar da wasu mutane da ɗanbindigar ke garkuwa da su.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp