fidelitybank

An kashe ƴan Bindiga sama da dubu 13 a mulkin Tinubu

Date:

Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa dakarun ƙasar sun kashe ‘ƴan ta’adda da masu aikata ta’asa a ƙasar sama da 13,543 a yankin arewa maso gabashin ƙasar tun bayan hawan shugaban ƙasar kan mulki kimanin shekara biyu da suka gabata.

Hakan na ƙunshe ne a cikin rahoto kan nasarorin da gwamnatin Tinubu ta samu a ɓangaren tsaro, wanda mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu ya bayar a ranar Talata.

Haka gwamnatin ƙasar ta bayyana cewa an ƙwato tare da lalata makamai sama da 11,118 a tsakankanin lokacin a yankin na ƙasar.

Ribadu ya ƙara da cewa iyalan ƴan Boko Haram da ISWAP sama da 124,408, sun miƙa wuya, sannan an ƙwato alburusai sama da 252,596.

Yankin arewa maso gabas dai ya ƙunshi jihohin Borno da Adamawa da Yobe da Bauchi da Gombe da Taraba, kuma yanki ne da ya shafe sama da shekara 10 yana fama da rikice-rikicen Boko Haram wanda ya yi sanadiyar mutuwar dubban mutane, tare da raba miliyoyi da muhallansu

naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp