fidelitybank

An kasa shayo kan ma’aikatan wutar lantarkin Kaduna

Date:

Kamfanin rarraba wutar lantarki na Kaduna Electric da ke da alhakin samar da lantarki ga jihohin Kaduna da Kebbi da Sokoto da Zamfara ya ce an gaza cimma matsaya tsakanin shugabanninsa da kungiyar ma’aikatan kamfanin duk da sanya bakin gwamnati da masu ruwa da tsaki.

Babban Jami’in sadarwar kamfanin, Abdulazeez Abdullahi a cikin wata sanarwar da ya fitar, ya ce duk da Æ™oÆ™arin samun matsaya tsakaninsu, ma’aikatan sun Æ™i amincewa su maido da wutar lantarki bayan katse ta tun ranar Litinin 3 ga watan Fabrairu.

Ya ce an gudanar da taruka tare da hukumomin tsaro da Gwamnatin jihar Kaduna ƙarƙashin jagoranci gwamnan jihar Uba Sani wanda mataimakiyarsa Hadiza Balarabe ta wakilta, inda ta bayyana yadda rashin wutar ke shafar fannin lafiya da kasuwanci ta kuma buƙace su da su mayar da wutar a lokaci ba tare da ɓata lokaci ba a lokacin tattaunawar.

A cewar sanarwar, an kuma yi zaman shiga tsakanin tare da babban lauyan Najeriya Sani Katu da kuma kwamishinan shari’ah na jihar Kaduna Sule Shuaibu SAN, sai dai haÆ™ar ta gaza cimma ruwa sakamakon sabbin buÆ™atu da Æ™ungiyar ma’aikatan ta gabatar.

Abdulazeez ya kuma ce: ”Wannan mataki da suka É—auka ya saÉ“a wa tabbacin da suka bai wa gwamnatin jihar Kaduna tun da farko na cewa za su mayar da wutar lantarkin a yayin da ake cigaba da tattaunawa.”

A farkon makon nan ne dai Kamfanin rarraba wutar lantarkin na Kaduna Electric ya ce ya sallami ma’aikata fiye da É—ari huÉ—u, wanda hakan ya kai ga shiga yajin aikin ma’aikatan tare da jefa alummomin jihohi huÉ—u cikin duhu.

Lamarin ya jefa al’umma cikin Æ™unci da haifar da asara ga masu sana’o’i.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama Æ´an Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na Æ™asa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta É—aure Matashin da ya shiga É—akin kwanan ÆŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp