fidelitybank

An karrama Sojojin da suka ki karbar cin hancin Miliyan 1.5

Date:

Rundunar soji ta musamman da ke da alhakin wanzar da zaman lafiya a jihar Filato ta karrama jami’an ‘Operation Safe Haven’ guda takwas, bisa kin karbar cin hancin Naira miliyan 1.5 daga wasu da ake zargin barayin shanu ne a jihar.

A wata sanarwa da kakakin rundunar, Kaftin Oya James ya fitar, ya ce jami’an 8 da aka tura sashin OPSH ta 4, sun kama wasu barayin shanu 30 na wani Shehu Umar a shingen binciken Bisichi da ke karamar hukumar Barkin Ladi a jihar.

Ya kara da cewa an yi awon gaba da shanun ne a garin Mangu kuma ana kai su zuwa wani wuri da ba a bayyana ba, yayin da dakarun rundunar da ke aikin tsagaita wuta suka tare su.

A cewar sanarwar, “wadanda ke cikin motar, Anas Usman dan shekara 20, da Gyang Cholly mai shekaru 42, nan take suka tunkari sojojin da nufin ba su cin hanci da rashawa tare da tabbatar da tsaron shanun da aka sace.

“An ki amincewa da neman kudin kuma an kama wadanda ake zargin, da kuma kudin da aka bayar na cin hanci.”

A cewar sanarwar, kwamandan rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo Janar Abubakar, yayin da yake mika kyautar kudi ga manyan jami’an, ya bukaci sauran jami’an tsaro da su ci gaba da nuna kyakykyawan hali da jajircewa wajen sauke nauyin da aka dora musu.

“Shugaban ma’aikatan OPSH, Brig. Gen. M.O. Agi, kwamandan ya kuma umarce su da su yi koyi da kyawawan halaye na ma’aikatan takwas,” in ji sanarwar.

the sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp