An Karkare babban taron sauyi yanayi na Majalisar Dinkin Duniya mai taken COP27, a kasar Masar ba tare da cimma matsaya kan rage gurbataccen iska ba, ko da yake an amince da ware kudade domin baiwa wasu kasashe su yaki dumamar yanayi.
An kammala Tattaunawar da aka shafe makonni biyu ana yi a wani wurin shakatawa na Sharm el-Sheikh dake kasar Masar, a ranar Lahadi tare da kulla wata muhimmiyar yarjejeniya kan bayar da kudade domin taimakawa kasashe masu rauni su tinkari mummunan tasirin yanayi, amma aka watse ba tare da cimma matsaya wajen rage garbatattacen hayaki da ake fitarwa ba.
Ministan yanayin Pakistan Sherry Rehman ta ce, bayan shefe sama da shekaru 30 ana gwagwarmaya daga karshe taron ya saurari koken kasashe marasa karfi wajen shere musu hawaye, wanda ke zama babban nasara da aka samu a Sharm el-Sheikh.
Babban magatakardar Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya bayyana farin cikinsa dangane da ci gaban da aka samu na samar da asusun asara da barnar tasirin sauyin yanayi, to sai dai kuma ya nuna damuwa kan gazawa wajen daukar matakan gaggawa na kawar da iska mai haifar da dumamar yanayi.
Matakin da Franministan Burtaniya Rishi Sunak ya yi gargadin cewa “dole sai an kara azama, yayin da shugaban Faransa Emmanuel Macron ya ba da shawarar sake wani taron a Paris domin amincewa da “sabon yarjejeniyar kunshin tallafin kudi” ga kasashe masu rauni gabanin taron na COP28 da za’a yi a Dubai na hadeddiyar daular larabawa.