fidelitybank

An kammala kwashe daliban Najeriya daga Sudan

Date:

Hukumomi a Najeriya sun tabbatar da kammala aikin kwashe ɗalibai ‘yan ƙasar da ke karatu a ƙasar Sudan Waɗanda ɓarkewar rikici tsakanin sojojin gwamnati da na RSF ya rutsa da su.

Ma’aikatar jin kai da kare afkuwar bala’i ta Najeriya da ta yi aikin kwashe daliban da haɗin gwiwar hukumar agajin gaggawa ta NEMA, da ofisoshin jakadancin Najeriya a ƙasashen Sudan da Masar ne suka sanar da hakan.

Babban sakatare a ma’aikatar jin kai da kare afkuwar bala’i a Najeriya Dakta Nasiru Sani Gwarzo ya shaida wa BBC cewa sai da aka bi matakan da suka dace domin tabbatar da kariyar ɗaliban, kafin a fara kwashe su.

Ya ce jirgin da ya sauka a ranar Asabar shi ne jirgi na 15 kuma shi ne na ƙarshe da ya ƙwaso ɗaliban Najeriyar da ke karatu a Sudan.

”Jirage huɗu na farko da suka kwaso ɗailbai kusan 800, sun taso ne daga ‘Aswan’ na ƙasar Masar, sai kuma ragowar 14 da suka taso daga Port Sudan”, in ji shi.

Dakta Gwarzo ya ce sun kwaso duka wani ɗan Najeriya da ke Sudan wanda ya nemi taimakonsu, kuma ya kasance yana da takardu.

Ya ce kashi 95 cikin 100 na mutanen da suka kwaso Dalibai ne da ke karatu a ƙasar ta Sudan.kashi 95 cikin 100 na mutanen da suka kwaso Dalibai ne da ke karatu a ƙasar ta Sudan.

Dakta gwarzo ya ce ”matsalar da muka samu da masu motocin bas-bas ce ta haddasa tsaikon da aka samu wajen ƙwashe ɗaliban a kan lokaci”.

Amma duk da haka a cewarsa babu ƙasar da ta iya kwaso adadin mutanen da suka kai na Najeriya a cikin wannan lokacin.

Game da matsayin karatun ɗaliban kuma dakta gwarzo ya ce sun tattauna da ma’aikatar ilimi ta ƙasar, wadda ya ce ta aiko musu da wani jadawali da za su rubuta sunayen ɗaliban, domin duba yiwuwar yadda za a tallafa wa ɗaliban.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp