fidelitybank

An kammala kwashe daliban Najeriya daga Sudan

Date:

Hukumomi a Najeriya sun tabbatar da kammala aikin kwashe ɗalibai ‘yan ƙasar da ke karatu a ƙasar Sudan Waɗanda ɓarkewar rikici tsakanin sojojin gwamnati da na RSF ya rutsa da su.

Ma’aikatar jin kai da kare afkuwar bala’i ta Najeriya da ta yi aikin kwashe daliban da haɗin gwiwar hukumar agajin gaggawa ta NEMA, da ofisoshin jakadancin Najeriya a ƙasashen Sudan da Masar ne suka sanar da hakan.

Babban sakatare a ma’aikatar jin kai da kare afkuwar bala’i a Najeriya Dakta Nasiru Sani Gwarzo ya shaida wa BBC cewa sai da aka bi matakan da suka dace domin tabbatar da kariyar ɗaliban, kafin a fara kwashe su.

Ya ce jirgin da ya sauka a ranar Asabar shi ne jirgi na 15 kuma shi ne na ƙarshe da ya ƙwaso ɗaliban Najeriyar da ke karatu a Sudan.

”Jirage huɗu na farko da suka kwaso ɗailbai kusan 800, sun taso ne daga ‘Aswan’ na ƙasar Masar, sai kuma ragowar 14 da suka taso daga Port Sudan”, in ji shi.

Dakta Gwarzo ya ce sun kwaso duka wani ɗan Najeriya da ke Sudan wanda ya nemi taimakonsu, kuma ya kasance yana da takardu.

Ya ce kashi 95 cikin 100 na mutanen da suka kwaso Dalibai ne da ke karatu a ƙasar ta Sudan.kashi 95 cikin 100 na mutanen da suka kwaso Dalibai ne da ke karatu a ƙasar ta Sudan.

Dakta gwarzo ya ce ”matsalar da muka samu da masu motocin bas-bas ce ta haddasa tsaikon da aka samu wajen ƙwashe ɗaliban a kan lokaci”.

Amma duk da haka a cewarsa babu ƙasar da ta iya kwaso adadin mutanen da suka kai na Najeriya a cikin wannan lokacin.

Game da matsayin karatun ɗaliban kuma dakta gwarzo ya ce sun tattauna da ma’aikatar ilimi ta ƙasar, wadda ya ce ta aiko musu da wani jadawali da za su rubuta sunayen ɗaliban, domin duba yiwuwar yadda za a tallafa wa ɗaliban.

the nation newspaper 
today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp