fidelitybank

An kama ‘yan Tawayen Kamaru a Taraba

Date:

Sojojin rundunar ta 6, sun kama mutane hudu da ake zargi da zama mambobin ‘yan tawayen Ambazonian a Taraba.

Ambazonia ƙungiya ce ta ‘yan tawayen da ke aiki a ƙasar makwabciyar kasa Jamhuriyar Kamaru.

A cikin wata sanarwa da Capt. Olubodunde Oni, ya fitar ranar Asabar a Jalingo daga Mataimakin Daraktan Yada Labarai na Sojojin Nijeriya, ya bayyana cewa an kama wadanda ake zargin ne a wani otel a garin Takum.

Sanarwar ta ce, bisa ga sahihin bayanan sirri da aka samu, an bi sawun masu laifin har lokacin da aka kama su. Kuma tuni suka amsa cewa suna daga cikin ƙungiyar ‘yan tawayen da ke kai hari da yaki da amfani da bindigogi tare da haɗin gwiwar wasu ‘yan Nijeriya.

Sanarwar ta kara da cewa an kwato wayoyi guda hudu daga hannun wadanda ake zargin, wadanda yanzu haka suna tsare yayin da ake cigaba da bincike.

Haka kuma, a cikin wani aiki na daban, bisa ga bayanan sirri da aka samu, sojojin da aka tura zuwa Natilde a yankin Bantaji na karamar hukumar Wukari sun kama wata mota wadda ke dauke da bututun mai guda 19 da aka sata wanda ke naɗe da tambarin Kamfanin Mai na kasa (NNPCL).

Sanarwar ta bayyana cewa, ci gaba da haɗin gwiwa tare da Hukumar Tsaro ta Ƙasa (NSCDC) a sashen Wukari ya kai ga samun ƙarin bututun 11, wanda ya haifar da jimillar bututun 30 da aka samu.

“An mika kayan da aka kwato ga NSCDC na sashen Wukari don ci gaba da bincike da kuma daukar matakin da ya kamata.

sahara hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp