fidelitybank

An kama ‘yan Najeriya da yunkurin lalata Dan Australiya

Date:

An kama mutum biyu a Najeriya saboda zarginsu da yunƙurin lalata da wani ɗalibi ɗan Australiya da ya hallaka kansa.

Ƴan sandan Australiya sun ce matashin da aka kashe ya yi musayar hotuna da wani mutum ta intanet kafin ya soma yin baraza da kuma neman kuɗi a hannunsa.

Bayan wani bincike da aka yi, an gano mutanen biyu da ake zargi a Najeriya inda za su fuskanci shari’a.

Ƴan sanda sun ce ɗabi’ar tilastawa mutum tura hotuna ta hanyar yin barazanar tona masa asiri musamman a tsakanin matasa na matuƙar ƙaruwa.

Ba a fitar da bayanan yaron – shekarunsa da kuma inda yake zaune a New South Wales ba, an yi haka domin kare iyalinsa.

Ƴan sanda a New South Wales sun ce waɗanda ake zargin suna tilasta tura masu hotunan jikin mutum ɗin matasa ne kuma sun ce sun yi barazanar tura hotunan matashin ga abokanai da kuma yan uwansa idan har ya ƙi biyansu dala 330.

“Saƙonnin sun yi muni. Sun matsa wa yaron lamba ya biya kuɗin,” in ji babban jami’in ɗan sanda da ke yaƙi da laifukan intanet, Mathew Craft, kamar yadda ya shaida wa jaridar Sydney Morning Herald.

Yaron ya mutu ne ta hanyar kashe kansa a yammacin ranar da abin ya faru s shekarar da ta gabata.

Ƴan sandan Australiya sun yi aiki tare da takwarorinsu a Afirka ta Kudu da Najeriya wajen zaƙulo mutanen da ake zargi da aika-aikar a Najeriya.

An gano shaidar da ke nuna matasan biyu sun yi ƙoƙarin karɓar kuɗi a hannun mutane cikin wayoyinsu, a cewar jaridar ta SMH. An tuhume su da zargin tilasta wa yaron ɗan Australiya kwanciya da su ba mutuwarsa ba. In ji BBC.

the nation newspaper nigeria today latest

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp