fidelitybank

An kama ‘yan Najeriya biyu a Kenya da zargin kisan kai

Date:

Yan sandan Kenya sun kama wasu maza biyu yan Najeriya saboda zargin suna da hannu a kisan wata daliba.

Sun bayyana gaban kotu sai dai ba a kai ga tuhumarsu ba.

An gano gawar daliba Rita Wdaeni mai shekara 20 cikin ladejin shara a wani gida da ke Nairobi babban birnin Kenya ranar 14 ga watan Janairu.

Kisan gillar da aka yi wa dalibar dai ya fusata al’ummar Kenya.

Sai dai kokon kanta tare da wayarta da sauran kayayyakinta, sun bata.

Kisan gillar ya sa an yi ta kiraye-kiraye a kara daukan mataki domin magance cin zarafin da ake yi wa mata.

Wasu yan Kenya hudu suma suna tsare game da kisan da kuma wani mutum wanda yake tafiye-tafiye da takardar fasfon Mozambique inda kuma aka damke shi yayin da yake shirin barin kasar.

Yan sanda sun bayyana sunayen mutanen biyu da ake zargi da William Ovie Opia da Johnbull Asbor.

Mr Opia yana da fasfon Najeriya wanda wa’adin amfaninsa ya cika kuma Mr Asbor ya rasa nasa fasfon shekaru biyu da suka gabata, kamar yadda yan sanda suka ce.

Yan sanda sun kwace kayayyaki da dama daga gidan mutanen da ake zargi ciki har da wuka da karamar adda da ake zargin sun yi amfani da su wajen kashe dalibar jami’ar tare da sauya mata kamanni, kamar yadda kafofin yada labaran Kenya suka rawaito yan sanda da cewa.

Mr Opia ya fada wa masu bincike cewa ya sayi addar ta intanet domin kare kansa, in ji jaridar Nation mai zaman kanta.

An kama mutanen biyu a Ndenderu, wani gari kai nisan kilomita 20 daga Nairobi kuma kusa da wata madatsa inda yan sanda suka gano kokon kan da ake zargi na Ms Waeni ne tare da wayoyinta da wasu kayayyakinta da suka bata.

Zuwa yanzu dai iyalin Ms Waeni basu kai ga tantance ko kan nata bane.

Iyalanta, a makon da ya wuce, sun ce wadanda ke da hannu a aika-aikar sun bukaci a biya su 500,000 a kudin Kenya kafin su saki Ms Waeni duk da cewa sun halaka ta.

Kungiyoyin kare hakkin bil adama da kungiyoyin kare hakkin mata sun shirya zanga-zanga a fadin kasar domin nuna fushinsu kan karuwar kisan mata da cin zarafin da ake masu.

An samu karuwar rahotannin kisan mata tun farkon wannan shekarar. Wani bincike da aka yi a 2022 ya gano cewa akalla kashi 34 cikin 100 na mata sun fuskanci cin zarafi a wasu lokuta na rayuwarsu.

nasarawa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka Æ´an Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar HaÉ—in kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran Æ™asa za ka mayar da kai ba zaÉ“en 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp