fidelitybank

An kama wani tsoho da zargin kashe ɗiyarsa

Date:

An kama wani dattijo mai shekaru 80, Dauda Ibrahim, bisa laifin yin garkuwa da diyarsa Sherifah mai shekaru 15 da haihuwa.

Jaridar DAILY POST ta rawaito cewa lamarin ya faru ne a karamar hukumar Idah ta jihar Kogi.

An ce wanda ake zargin ma’aikaci ne na Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Tarayya, Idah, a sashin ayyuka da kashe gobara.

Ana zarginsa da aikata wannan danyen aiki tare da wasu mutane biyu Isah Adams da Adah daya.

Wata majiya ta bayyana cewa an yi garkuwa da mamaciyar, Sherifah a ranar 4 ga watan Agusta, 2022, a gidansu dake Okenya, kan titin Itayi, a karamar hukumar Igalamela/Odolu ta jihar.

Majiyar ta kara da cewa an gano gawar yarinyar a cikin wani kabari mara zurfi kwanaki kadan bayan bacewar ta, tare da yanke jiki, yayin da wasu muhimman gabobin suka bace.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Williams Ayah, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya bayyana cewa wanda ake zargin da wadanda ake zarginsa da shi suna hannun ‘yan sanda a halin yanzu.

A cewar PPRO na jihar, kwamishinan ‘yan sandan, CP Edward Egbuka ya bayar da umarnin a mika lamarin zuwa sashin binciken manyan laifuka da ke Lokoja domin ci gaba da bincike.

www.legit.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp