Hukumar tsaro ta Amotekun a jihar Ekiti, ta kama wani mutum mai suna Celestine Nwoha mai shekaru 50 da takardun kudi na bogi.
Da yake yiwa manema labarai jawabi a Ado Ekiti, kwamandan rundunar, Birgediya Joe Komolafe mai ritaya, ya ce an kama wanda ake zargin ne a Omuo Ekiti, karamar hukumar Ekiti ta Gabas.
Karanta Wannan: Rashin kudi na CBN shi ne COVID-23 – Ganduje
Ya ce: “Wanda ake zargin ya je wani yanki a Omuo ya fara kashe kudin kafin mu samu labari muka bi shi.
“Ya ce ya kware wajen siyan kola da kola mai daci, inda ya ce an biya shi da tsabar kudi a Legas.
“Da aka yi masa tambayoyi, ya amsa laifinsa, ya ce an ba shi N250,000 daga wata masana’anta a Legas, amma N100,000 kawai aka samu a tare da shi kamar yadda ya kashe wasu.”
Komolafe ya ce rundunar za ta mika shi ga ‘yan sanda domin gudanar da bincike.
Birgediya Komolafe ya bukaci jama’a da su yi taka-tsan-tsan, musamman a lokacin da ake fama da tabarbarewar kudi, don ka da a fada masu.