fidelitybank

An kama wanda ya kware da satar mota a Kaduna

Date:

Rundunar ‘yan sanda a jihar Kaduna ta ce, jami’anta sun kama wani da ake zargi da satar mota tare da gano wani dan fashi da makami a jihar.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, ASP Mansir Hassan, ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a a Kaduna.

Hassan ya ce, “A ranar 27 ga Mayu, da misalin karfe 1830, jami’an mu sun samu labari daga wani Basamariye nagari.

“Wani mutum ya ruwaito cewa an nemi ya taimaka wajen karbar Lexus LX470 Jeep daga kanikanci.”

A cewarsa, da karbar motar ya yi zargin sata ne, kuma ba tare da bata lokaci ba ya kai rahoto ga ‘yan sanda.

Hassan ya ce bayan rahoton an gano motar tare da kawo ofishin ‘yan sanda na Magaji Gari da ke cikin babban birnin Kaduna.

“An gudanar da bincike, inda aka gano bayanan motar da ke dauke da sunan mai shi, tare da lambar wayarsa.

“Da aka tuntubi mai gidan ya bayyana cewa wasu ‘yan bindiga biyar ne suka kwace masa motar da bindiga a gidansa da ke Utako, Abuja,” inji shi.

Hassan ya kara da cewa ‘yan sanda sun gudanar da bincike tare da samun nasarar cafke wanda ake zargin mai suna Mubarak Kabiru daga Kano a kan hanyar Alkali, Kaduna.

Ya kara da cewa, “Binciken da aka yi a dakinsa da ke Otal din Ishacool, Kabala Doki, Kaduna, an gano wani ma’aikacin da ke hana sa-ido.”

sun newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp