fidelitybank

An kama wanda suka kashe ‘yar siyasa mai yin TikTok

Date:

‘Yan sanda a India sun ce sun kama wasu mutum biyu da ake zargi da hannu a kisan da aka yi wa fitacciyar ‘yar siyasar nan kuma tsohuwar mai yin TikTok Sonali Phogat.

An kama mutanen ne bayan sakamakon gwajin gawar da aka yi ya nuna cewa kasheta aka yi saboda an ga raunuka a jikinta.

Sonali Phogat, mai kimanin shekara 42 da haihuwa, ta kai ziyara ne birnin Goa, in da aka kasheta a ranar 22 ga watan Augustan da muke ciki. In ji BBC,

Rahotanni farko sun ce bugawar zuciya ne ya yi sanadin mutuwarta, to amma daga bisani da aka yi wa gawarta gwaji aka gano kasheta aka yi.

Dan uwanta dai ya bayyana wa ‘yan sandan da ke bincike sunan wasu mataimakanta biyu in da ya ce sun rinka yi mata barazana da wani hoton bidiyo da bata son a gani.

Ya ce, mutanen sun yi mata fyade daga bisani kuma suka kasheta, sannan suka sace mata abubuwa da suka hada da waya da kuma katunanta na cire kudi wato ATM.

Iyalan marigayiyar sun ce kafin kisan nata sai da ta kirasu suka yi magana kuma sun ji ta kamar akwai damuwa a tare da ita.

latest legit news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp