fidelitybank

An kama riƙaƙƙun ƴan fashin da suka addabi jihar Nasarawa

Date:

Rundunar ƴan sandan jihar Nasarawa sun kama wasu mutane biyu da ake zargi ƴan fashi da makami ne da ake kira ‘One Chance’ waɗanda kuma suke gudanar da harkokinsu a babbar hanyar Akwanga zuwa Keffi.

Kakakin rundunar Ramhan Nansel ne ya tabbatar da haka cikin wata sanarwa da ya fitar inda ya ce binciken farko da aka gudanar ya nuna mutanen da ake zargi suna bayyana kansu a matsayin direbobin tasi domin ɗaukan fasinjoji, sannan su kai su wani waje tare da kwashe masu kuɗinsu da kayayyakinsu, sannan kuma su yasar da fasinjojin su kuma tsere.

Mutanen da ake zargi sun tabbatar da aika-aikatr da suke inda suka ce sun shafe fiye da shekara 10 suna yi wa mutane fashi.

Sun ƙara da cewa ko a baya-bayan nan an sako su daga gidan gyaran hali na Shendam a jihar Filato saboda aikata makamancin wannan laifin bayan da suka kammala hukuncin da aka yanke masu.

Kayan da aka gano a hannunsu akwai mota ƙirar Toyota da wata adda da guduma.

Kwamishinan ƴan sanda na jihar ta Nasarawa Umar Shehu Nadada ya bayar da umarnin a gurfanar da mutanen biyu gaban kotu da zarar an kammala bincike.

Ya kuma bai wa jama’a tabbaci cewa rundunar za ta ci gaba da aikin kakkaɓe miyagun laifuka a jihar, yana mai neman haɗin kansu wajen cimma ƙudirin.

tribune newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp