fidelitybank

An kama mutumin da ya kashe Biri a Awka

Date:

A ranar Larabar da ta gabata ne ’yan kabilar Awka suka kama wani matashi mai matsakaicin shekaru bisa laifin kashe biri.

An san birai dabbobi ne masu tsarki a daukacin masarautar Awka, kuma ana kallon kashe su a matsayin wani abu na ibada.

‘Yan asalin Awka na da wani biki da aka sadaukar domin bautar gunkin Imo Awka, wanda ke da wurin ibada a yankin Amaenyi da ke garin.

A daukacin masarautar, ba wani abin mamaki ba ne a ga birai suna tsalle-tsalle a cikin wuraren mutane ba tare da tsangwama ba.

Mutumin da aka kama a ranar Laraba da laifin kashe dabbar, an gan shi a cikin wani faifan bidiyo da ya yi ikirarin cewa ya rayu a Awka tsawon shekaru 24, kuma yana sane da cewa mutanen Awka ba su yarda a kashe ko cin naman birai ba.

Ya bayyana cewa, ba da gangan ya kashe biri ba, a’a, ya tada tarko ne a cikin daji, yana fatan ya kashe sauran naman daji da za a yi amfani da shi wajen cin abinci, amma abin takaici, biri ne ya makale.

Ya ce: “Na san na aikata, don Allah kar ka kashe ni, amma za ka iya kai ni duk inda kake so.”

‘Yan asalin da ke yi masa tambayoyi daga baya sun ga wasu dalilai a tare da shi, kuma suka ce masa ba za a kashe shi ba, amma al’umma za su dauki matakin farantawa Ubangijin kasa rai saboda abin da ya yi don kauce wa abin da ya faru.

Ba a dai bayyana inda mutumin ya fito ba, ko kuma sunan sa.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp