Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Ribas, sun kama wasu mutane 3 da ake zargin ‘yan kungiyar asiri ne da ke addabar al’ummomin yankin Ogoni.
An kuma samu wata bindiga da aka kera a cikin gida daga hannun wadanda ake zargin.
Jami’ar hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, Grace Iringe Koko a wata sanarwa da ta fitar a ranar Larabar da ta gabata, ta ce jami’an rundunar da ke yaki da kungiyar asiri sun kai farmakin ne bayan wani rahoto daga al’ummar Gure da ke karamar hukumar Khana ta jihar.
An gudanar da aikin ne a ranar 9 ga watan Janairu lokacin da jami’an ‘yan sandan suka far wa sansanin ‘yan kungiyar asiri.
A cewar sanarwar, wadanda aka kama sun hada da Kensuanu Loveday wanda aka ce shi ne mai zartar da hukuncin kisa ga ‘yan kungiyar asiri, Myimaka Only da Junior Mbo.
Kakakin ‘yan sandan ya ce za a gurfanar da wadanda ake zargin zuwa kotu bayan bincike.
Ta sake jaddada kudurin hukumar na rage aikata laifuka da aikata laifuka cikin kankanin lokaci.