‘Yan sanda a jihar Filato sun ce, an kama manyan waɗanda ake zargi tara a sabbin hare-haren da aka kai a yankin Mangu na Jihar.
Aƙalla mutane 50 ne aka ruwaito an kashe a cikin kwanaki biyu da aka dauka ana gwabza faɗa tsakanin ƙabilu.
Wasu mahara ɗauke da makamai dai sun kai hari a ƙauyukan da ke kusa da garin Mangu a ranar Larabar da ta gabata, kwana guda bayan da aka ƙona masallatai da majami’u a arangama tsakanin kabilu biyu da ke gaba da juna.
Mai magana da yawun rundunar sojin Najeriya Janar Edward Buba, ya ce an tura dakaru na musamman zuwa wuraren da ke fama da tashe-tashen hankula a jihar domin shawo kan lamarin.